Laraba 17 Yuni 2026 - 21:58
Fansar Jinin Shahidin Jagora Zai Tabbata Ne Kawai Da Kawar Da Azzalumai Da Kuma Korar Amurka Daga Yankin Gabas Ta Tsakiya 

Hauza/ Limamin Masallacin Juma’ar Qazvin ya bayyana cewa, muna neman ɗaukar fansar jinin Shahidin jagoranmu, kuma hakan ba zai taba tabbata ba sai da lalata rundunar kafirci da girman kai, da kuma korar dukkan sojojin Amurka daga yankin.

A rahoton wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Hauza a Qazvin, Hujjatul Islam wal Muslimin Hussain Muzaffari, a zama na bakwai na kwamitin tallafawa yaki da sake gina yankunan da abin ya shafa na lardin Qazvin, ya ce: "Ina mika ta'aziyyata ga kowannenku kan zuwan watan Muharram da kuma ranakun shahadar Imam Hussain (AS). Ina fatan dukkanmu mu sami damar bauta da kuma yin makokin Imam Hussain (AS)."

Ya ci gaba da cewa: "Muna girmama tunawa da Imam Khumaini (RA), Shahidin jagoran juyin juya halin Musulunci, da kuma dukkan shahidanmu, musamman shahidan yaƙin da aka yi a baya."

Hujjatul Islam wal Muslimin Muzaffari ya bayyana cewa: "Da hikima da jagorancin Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci, da goyon bayan jama'a, da jajircewar sojoji, da kuma kokarin tawagar diflomasiyya, mun samu babbar nasara akan maƙiya masu taurin kai da laifuka."

Wakilin Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci a lardin Qazvin ya jaddada cewa: "Yarjejeniyar da ake magana a kai kuma take gab da rattaba hannu, duk da korafe-korafen da wasu za su iya yi, babu shakka nasara ce ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran."

Ya bayyana rashin jin daɗi da kuma tashin hankalin da haramtacciyar kasar Isra'ila ta nuna dangane da wannan yarjejeniya a matsayin alamar nasarar Iran ta Musulunci, inda ya kara da cewa: "Maƙiya ba su kai ga cimma ko daya daga cikin burinsu ba, kuma an tilasta musu amincewa da wannan yarjejeniya ne sakamakon karfin Jamhuriyar Musulunci da kuma jama'arta."

Shugaban majalisar ilimi ta lardin Qazvin ya ce: "Dukkanmu mun san cewa maƙiya ba su da amana ko kaɗan, ko da an rattaba hannu kan yarjejeniyar, bai kamata mu zauna lafiya ba. Ba mu da zaman lafiya da makiya, kuma wannan yarjejeniya mataki ne kawai na gwagwarmayarmu da su."

Limamin masallacin Juma’a na Qazvin ya bayyana cewa: "Wannan yaƙi ne na rayuwa da mutuwa; muna neman ganin bayan maƙiya ne, kuma su ma lokaci zuwa lokaci suna yin irin wannan mafarkin a kanmu."

Ya ci gaba da cewa: "Muna neman ɗaukar fansar jinin Shahidin shugabanmu ne wanda ya yi shahada, wanda hakan ba zai tabbata ba sai da lalata rundunar kafirci da girman kai, da kuma korar dukkan sojojin Amurka daga yankin."

Wakilin jama'ar Qazvin a majalisar kwararru (Assembly of Experts) ya tunatar da cewa: "Bisa la'akari da yanayin da ake ciki, bai kamata mu dauki aikin wannan kwamiti a matsayin wanda ya ƙare ba. Yiwuwar faruwar rikicin soji bai kare ba, kuma akwai yiwuwar mu sake shiga yaki da maƙiya, don haka dole ne mu ci gaba da gudanar da ayyukanmu da dukkan karfi."

Hujjatul Islam wal Muslimin Muzaffari ya bayyana cewa: "Yan uwanmu a Lebanon da sauran wurare suna matukar buƙatar taimakonmu, don haka kada mu yi sakaci wajen hakan."

A wani ɓangare na jawabin nasa, da yake magana kan shirye-shiryen jana'izar jagoran juyin juya halin Musulunci wanda ya yi shahada, ya jaddada cewa: "Bisa la'akari da cewa ana gab da gudanar da jana'izar shugaban juyin juya halin Musulunci, Ayatullah Khamenei (QS) da iyalansa masu girma, ya zama wajibi kowa ya tashi tsaye. An riga an gudanar da taruka dangane da hakan, kuma an yanke shawarar cewa kwamitin tallafawa yaki da sake gina yankunan da abin ya shafa na lardin Qazvin ne zai tattara taimakon jama'a."

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha